Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

M. Sh 32:36-44 Littafi Mai Tsarki (HAU)

36. Ubangiji zai ɗauka wa jama'arsa fansa,Zai ji ƙan bayinsa,Sa'ad da ya ga ƙarfinsu ya kāsa,Ba kuma wanda ya ragu, bawa ko ɗa.

37. Sa'an nan zai ce, ‘Ina gumakansu,Dutse wanda suka nemi mafaka gare shi,

38. Waɗanda suka ci kitsen hadayunsu,Suka sha ruwan inabin hadayarsu ta sha?Bari su tashi su taimake ku,Bari su zama mafaka!

39. “ ‘Ku duba fa, ni ne shi,Ba wani Allah, banda ni,Nakan kashe, in rayar,Nakan sa rauni, nakan kuma warkar,Ba wanda zai cece su daga hannuna.

40. Na ɗaga hannuna sama,Na rantse da madawwamin raina,

41. Sa'ad da na wasa takobina mai walƙiya,Na riƙe shi da hannuna don yin hukunci,Zan ɗauki fansa a kan magabtanaZan sāka wa maƙiyana.

42. Zan sa kibauna su bugu da jini,Takobina zai ci nama,Da jinin kisassu da na kamammu,Da ƙoƙon kan shugabannin maƙiya.’

43. “Ya ku al'ummai, ku yabi jama'arsa,Gama zai rama wa bayinsa saboda jininsu,Zai ɗauki fansa a kan magabtansa,Zai tsarkake ƙasar jama'arsa.”

44. Sai Musa da Joshuwa ɗan Nun suka zo, suka hurta dukan kalmomin wannan waƙa a kunnen jama'a.

Karanta cikakken babi M. Sh 32