Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

M. Sh 2:32-37 Littafi Mai Tsarki (HAU)

32. Sai Sihon da mutanensa suka fita su gabza yaƙi da mu a Yahaza.

33. Ubangiji Allahnmu ya bashe shi a hannunmu, muka ci nasara a kansa, da 'ya'yansa, da dukan mutanensa.

34. Muka ci dukan garuruwansa, muka hallaka kowane gari, da mata, da maza, da yara, ko ɗaya bai ragu ba.

35. Sai dabbobi ne kaɗai da dukiyar garuruwan da muka ci, su ne muka kwashe ganima.

36. Daga Arower wadda take gefen kwarin kogin Arnon, zuwa Gileyad har ma da garin da yake cikin kwarin, Ubangiji Allahnmu ya ba da dukan kome a gare mu. Ba birnin da ya gagare mu.

37. Amma ba ku kusaci ƙasar Ammonawa ba, wato ƙasar da take a kwarin kogin Yabbok, da garuruwan ƙasar tuddai, da wuraren da Ubangiji Allahnmu ya hana mu.”

Karanta cikakken babi M. Sh 2