Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

M. Sh 1:30-36 Littafi Mai Tsarki (HAU)

30. Ubangiji Allahnku wanda yake tafiya tare da ku, shi kansa zai yi yaƙi dominku kamar yadda ya yi muku a Masar a kan idonku.

31. Kun ma ga yadda Ubangiji ya bi da ku cikin jeji kamar yadda mutum yakan bi da ɗansa, a dukan tafiyarku har zuwa wannan wuri.’

32. Amma ko da yake ya yi muku haka duk da haka ba ku dogara ga Ubangiji Allahnku ba.

33. Shi wanda ya bishe ku, ya nuna muku inda za ku yi zango. Da dare yakan nuna muku hanya da wuta, da rana kuma yakan bi da ku da girgije.”

34. “Ubangiji kuwa ya ji maganganunku, sai ya yi fushi, ya rantse, ya ce,

35. ‘Daga cikin mutanen wannan muguwar tsara ba wanda zai ga ƙasan nan mai albarka wadda na rantse zan ba kakanninku,

36. sai dai Kalibu ɗan Yefunne, shi kaɗai ne zai gan ta. Zan ba shi da 'ya'yansa ƙasar da ƙafarsa ta taka, gama shi ne ya bi Ubangiji sosai.’

Karanta cikakken babi M. Sh 1