Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Kid 32:37-42 Littafi Mai Tsarki (HAU)

37. Ra'ubainawa kuwa suka gina Heshbon da Eleyale, da Kiriyatayim,

38. da Nebo, da Ba'al-meyon, da Sibma.

39. Mutanen Makir, ɗan Manassa, suka tafi Gileyad, suka ci ta da yaƙi, suka kori Amoriyawan da suke cikinta.

40. Sai Musa ya ba mutanen Makir, ɗan Manassa, Gileyad, suka zauna ciki.

41. Yayir, ɗan Manassa, ya tafi ya ci ƙauyukansu da yaƙi, suka ba su suna Hawot-yayir.

42. Noba kuma ya tafi ya ci Kenat da ƙauyukanta da yaƙi, ya ba ta suna Noba bisa ga sunansa.

Karanta cikakken babi L. Kid 32