Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Kid 32:28-38 Littafi Mai Tsarki (HAU)

28. Sai Musa ya yi wa Ele'azara firist, da Joshuwa ɗan Nun, da shugabannin gidajen kakannin kabilan mutanen Isra'ila kashedi a kansu,

29. ya ce, “Idan kowane soja na Gadawa da Ra'ubainawa zai haye Urdun tare da ku don yaƙi har an ci ƙasar dominku, to, sai ku ba su ƙasar Gileyad ta zama mallakarsu.

30. Amma idan ba su haye tare da ku da shirin yaƙi ba, to, sai ku ba su gādo tare da ku a cikin ƙasar Kan'aniyawa.”

31. Gadawa da Ra'ubainawa kuwa suka ce, “Kamar yadda Ubangiji ya ce wa barorinka, haka za mu yi.

32. Za mu haye da shirin yaƙi a gaban Ubangiji zuwa cikin ƙasar Kan'aniyawa, amma za mu sami gādonmu a wannan hayin Urdun.”

33. Sa'an nan Musa ya ba Gadawa, da Ra'ubainawa, da rabin mutanen Manassa, ɗan Yusufu, mulkin Sihon, Sarkin Amoriyawa, da mulkin Og, Sarkin Bashan, wato ƙasar da biranenta da karkaransu.

34. Sai Gadawa suka gina Dibon, da Atarot, da Arower,

35. da Atarot-shofan, da Yazar, da Yogbeha,

36. da Bet-nimra, da Bet-aram su zama birane masu garu da shinge don dabbobi.

37. Ra'ubainawa kuwa suka gina Heshbon da Eleyale, da Kiriyatayim,

38. da Nebo, da Ba'al-meyon, da Sibma.

Karanta cikakken babi L. Kid 32