Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Kid 31:8-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Suka kashe har da sarakuna biyar na Madayanawa, da Ewi, da Rekem, da Zur, da Hur, da Reba. Suka kuma kashe Bal'amu ɗan Beyor.

9. Isra'ilawa suka kwashi mata da yaran Madayanawa bayi. Suka washe shanunsu, da tumakinsu da dukan dukiyarsu ganima.

10. Suka kuma ƙone dukan biranen zamansu da dukan san saninsu da wuta.

11. Da mutum da dabba sun kwashe su ganima.

12. Suka kawo bayin da ganimar a wurin Musa, da Ele'azara firist, da taron jama'ar Isra'ila a zango a filayen Mowab a Kogin Urdun daura da Yariko.

13. Sai Musa da Ele'azara firist, da shugabannin taron jama'ar Isra'ila suka fita zango su tarye su.

Karanta cikakken babi L. Kid 31