Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Kid 26:8-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Fallu ya haifi Eliyab.

9. 'Ya'yan Eliyab, maza su ne Yemuwel, da Datan, da Abiram. Datan da Abiram ne aka zaɓa daga cikin taron jama'ar, suna cikin ƙungiyar Kora wadda ta tayar wa Musa da Haruna, har ma da Ubangiji.

10. Ƙasa kuwa ta buɗe ta haɗiye su tare da Kora. Wuta kuma ta cinye sauran mutanen ƙungiyar, mutum ɗari biyu da hamsin suka mutu. Suka zama abin faɗakarwa.

11. Amma 'ya'yan Kora ba su mutu ba.

12. 'Ya'yan Saminu, maza, bisa ga iyalansu, su ne Yemuwel, da Yamin, da Yakin,

13. da Zohar, da Shawul. Waɗannan su ne iyalan kabilar Saminu.

14. Yawansu ya kai mutum dubu ashirin da biyu da ɗari biyu (22,200).

15. Zuriyar Gad bisa ga iyalansu, su ne Zifiyon, da Haggi, da Shuni,

16. da Ezbon, da Eri,

17. da Arodi, da Areli.

18. Waɗannan su ne iyalan kabilar Gad. Yawan mutanensu ya kai dubu arba'in da ɗari biyar (40,500).

Karanta cikakken babi L. Kid 26