Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Kid 20:22-23-29 Littafi Mai Tsarki (HAU)

22-23. Sai taron jama'ar Isra'ila suka kama tafiya daga Kadesh, suka je Dutsen Hor, a kan iyakar ƙasar Edom. Ubangiji kuwa ya ce wa Musa da Haruna a can,

24. “Haruna ba zai shiga ƙasar da na alkawarta zan ba Isra'ila ba, zai mutu, gama ku biyun nan kuka tayar wa umarnina a Meriba.

25. Ka kawo Haruna da ɗansa, Ele'azara, bisa Dutsen Hor.

26. Ka tuɓe wa Haruna rigunansa na firist, ka sa wa ɗansa, Ele'azara. Haruna zai mutu can.”

27. Musa kuwa ya yi yadda Ubangiji ya umarta. Suka hau bisa Dutsen Hor a idon dukan taron jama'a.

28. Sai Musa ya tuɓe wa Haruna rigunansa na firist ya sa wa Ele'azara ɗan Haruna. Haruna kuwa ya rasu a kan dutsen. Sa'an nan Musa da Ele'azara suka sauko daga kan dutsen.

29. Sa'ad da dukan jama'a suka ga Haruna ya rasu, sai duka suka yi makoki dominsa har kwana talatin.

Karanta cikakken babi L. Kid 20