Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Fir 8:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ubangiji ya ce wa Musa,

2. “Ɗauki Haruna da 'ya'yansa maza, da rigunan, da man keɓewa, da bijimi na yin hadaya don zunubi, da raguna biyu, da kwandon abinci marar yisti.

3. Ka kuma tattara jama'a duka a ƙofar alfarwa ta sujada.”

4. Musa kuwa ya yi yadda Ubangiji ya umarce shi. Jama'ar kuwa suka tattaru a ƙofar alfarwa ta sujada.

5. Musa ya faɗa wa taron jama'ar cewa “Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta a yi.”

Karanta cikakken babi L. Fir 8