Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Fir 18:1-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ubangiji kuma ya ce wa Musa

2. ya faɗa wa mutanen Isra'ila cewa, “Ni ne Ubangiji Allahnku.

3. Kada ku yi kamar yadda suke yi a ƙasar Kan'ana inda nake kai ku. Kada ku kiyaye dokokinsu.

4. Amma ku bi ka'idodina, ku yi tafiya a cikinsu, gama ni ne Ubangiji Allahnku.

5. Domin haka sai ku kiyaye dokokina da ka'idodina waɗanda ta wurin kiyaye su mutum zai rayu. Ni ne Ubangiji.”

6. Ubangiji ya ba da waɗannan ka'idodi kuma. Kada kowane mutum ya kusaci 'yar'uwarsa don ya kwana da ita. Ya ce, “Ni ne Ubangiji.”

Karanta cikakken babi L. Fir 18