Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

K. Mag 8:2-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. Tana tsaye bisa kan tuddai a bakin hanyaDa a mararraban hanyoyi.

3. A ƙofofin shiga birni, tana kira,

4. “Ina roƙonku, ya ku, 'yan adam,Ina kiran kowane mutum da yake a duniya.

5. Ba ku balaga ba? To, ku balaga.Ku wawaye ne? Ku koyi hankali.

6. Ku kasa kunne ga jawabina mafi kyau,Dukan abin da na faɗa muku daidai ne.

7. Abin da na faɗa gaskiya ne,Ƙarairayi abin ƙi ne a gare ni.

8. Kowane abu da na faɗa gaskiya ne,Ba wani abu da yake na laifi ko na ruɗawa.

9. Ga mutum mai basira, dukan abu ne a sarari,Ga wanda aka sanar da shi sosai, abu ne a sawwaƙe.

10. Ka zaɓi koyarwata fiye da azurfa,Ka zaɓi ilimi fiye da zinariya tsantsa.

11. “Ni ce hikima, na fi lu'ulu'ai,Cikin dukan abin da kake so, ba kamata.

12. Ni ce hikima, ina da basira,Ina da ilimi da faɗar daidai.

13. Ƙin mugunta shi ne tsoron Ubangiji,Na ƙi girmankai, da fāriya, da mugayen hanyoyi,Da maganganu na ƙarya.

14. Nakan shirya abin da zan yi, in kuwa yi shi.Ina da fahimi, ina da ƙarfi.

Karanta cikakken babi K. Mag 8