Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

K. Mag 5:9-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

9. Idan kuwa kun yi, girmamawar da ake yi muku za ta zama ta waɗansu. Za ku yi mutuwar ƙuruciya ta hannun mutane marasa imani.

10. Hakika, baƙi za su kwashe dukan dukiyarku, abin da kuka sha wahalar samu kuma zai zama rabon wani dabam.

11. Za ku kwanta kuna nishi a kan gadon mutuwa, namanku da tsokokinku za su zagwanye.

12. Sa'an nan za ku ce, “Me ya sa ban taɓa koyo ba? Me ya sa ban yarda wani ya kwaɓe ni ba?

13. Ban kasa kunne ga malamaina ba. Ban mai da hankalina gare su ba.

14. Farat ɗaya sai aka kunyatar da ni a bainar jama'a.”

15. Ka yi aminci ga matarka, ka ƙaunace ta ita kaɗai.

Karanta cikakken babi K. Mag 5