Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

K. Mag 29:7-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Adali yana sane da hakkin matalauta, amma mugun bai san wannan ba.

8. Ashararai sukan sa wa birni wuta, amma masu hikima sukan kwantar da hasala.

9. Idan gardama ta shiga tsakanin mai hikima da wawa, sai wawa ya yi ta fushi, ko kuwa ya yi ta dariya, gardamar dai ba za ta ƙare ba.

10. Mutane masu kisankai suna ƙin amintaccen mutum, amma adalai za su kiyaye ransa.

11. Wawa yakan nuna fushinsa ko yaushe, amma mutum mai hikima yakan kanne fushinsa.

12. Idan mai mulki yana kasa kunne ga maganganun ƙarya, dukan ma'aikatansa za su zama maƙaryata.

13. Matalauci da azzalumi suna tarayya a abu ɗaya, wato dukansu Ubangiji ne yake ba su ganin gari.

14. Idan sarki yana yi wa talakawa shari'ar gaskiya, zai daɗe yana mulki.

15. Horo da tsautawa suna ba da hikima, amma yaron da aka sangarta zai jawo wa mahaifiyarsa kunya.

16. Sa'ad da mugaye suke mulki, laifofi suka ƙaru, amma adalai za su ga faɗuwar waɗannan mutane.

17. Ka hori ɗanka zai daɗaɗa maka rai, ya kuma faranta maka zuciya.

18. Inda ba a bin faɗar Allah, jama'a za su kangare, amma mai farin ciki ne wanda yake kiyaye dokar Allah.

19. Bara ba ya horuwa ta wurin magana kawai, gama ko da ya fahimta ma, ba zai kula ba.

20. Ka ga mutum mai garajen yin magana? To, gara a sa zuciya ga wawa da a sa zuciya gare shi.

21. Baran da aka shagwaɓa tun yana yaro, a ƙarshe zai ɗauki kansa tankar magājin gida.

Karanta cikakken babi K. Mag 29