21. Idan maƙiyinka yana jin yunwa ka cishe shi, idan yana jin ƙishi ka ba shi abin sha.
22. Za ka sa ya sha kunya, Ubangiji kuma zai sāka maka.
23. Iskar arewa takan kawo ruwan sama, haka kuma jita-jita takan kawo fushi.
24. Gara zama a saƙo da zama a gida ɗaya tare da mata mai mita.
25. Jin labari mai daɗi wanda ba ka zato, yana kamar shan ruwan sanyi ne a sa'ad da ka sha rana kana jin ƙishi.