Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

K. Mag 21:6-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Dukiyar da aka tara ta hanyar rashin gaskiya takan ƙare nan da nan, takan kuma kai ga mutuwa.

7. Mugaye, tasu ta ƙare saboda muguntarsu, gama sun ƙi yin abin da yake daidai.

8. Mutane masu laifi sukan bi ta karkatacciyar hanya, marasa laifi kuwa suna aikata abin da yake daidai.

9. Gara zama a saƙo da zama a gida ɗaya tare da mace mai mita.

10. Mugaye sun zaƙu su aikata mugunta, ba su yi wa kowa jinƙai.

11. Sa'ad da aka hukunta mai girmankai, ko marar tunani yakan koyi wani abu, mutum mai hikima yakan koyi abin da ake koya masa.

12. Adali ya san tunanin mugaye, yakan kuwa zama sanadin lalacewarsu.

13. Idan ka ƙi jin kukan matalauci, naka kukan da kake yi na neman taimako, ba za a ji ba.

14. Kyauta a asirce takan kwantar da zuciyar wanda yake fushi da kai.

15. Sa'ad da aka yi adalci mutanen kirki sukan yi murna, amma mugaye sukan yi baƙin ciki.

16. Mutuwa tana jiran wanda ya ƙi bin hanyar hankali.

17. Sa kai cikin nishaɗi, wato shan ruwan inabi, da cin abinci mai tsada, ba zai bar ka ka tara dukiya ba.

18. Wahalar da mugaye suke so su jawo wa mutanen kirki, za ta koma kansu.

19. Gara ka zauna a hamada, da ka zauna tare da mace mai mita, mai yawan kai ƙara.

20. Mutane masu hikima suna zaune da wadata da nishaɗi, amma wawaye da zarar sun sami kuɗi sukan kashe su nan da nan.

21. Ka yi alheri ka yi aminci, za ka yi tsawon rai waɗansu kuma za su girmama ka, su yi maka abin da yake daidai.

Karanta cikakken babi K. Mag 21