Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

K. Mag 20:10-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Allah yana ƙin masu ma'aunin algus.

11. Ayyukan da saurayi yake yi suke bayyana yadda yake, kana iya sani ko shi amintacce ne, mai nagarta.

12. Ubangiji ya ba mu ido don mu gani, ya ba mu kunne don mu ji.

13. Idan barci ne sana'arka za ka talauce. Ka yi ta aiki za ka sami wadataccen abinci.

14. Mai saye yakan yi kukan tsada a kullum, amma yakan tafi ya yi ta fāriya a kan ya iya ciniki.

15. In ka san abin da kake faɗa, kana da wani abu wanda ya fi zinariya da lu'ulu'ai tamani.

16. Sai wawa kaɗai yake ɗaukar lamunin biyan basusuwan da baƙo ya ci, ya kamata a karɓi dukiyarsa jingina.

17. Abin da ka samu ta hanyar zamba kakan ji daɗinsa kamar abinci mai kyau, amma ko ba jima ko ba daɗe zai zama kamar yashi cike da bakinka.

18. Ka nemi kyakkyawar shawara za ka yi nasara, kada ka jefa kanka cikin yaƙi ba tare da shiri ba.

19. Mai baza jita-jita ba shi da asiri, ka yi nesa da mai yawan surutu.

20. Idan ka zagi iyayenka, za ka mutu kamar fitilar da ta mutu cikin duhu.

21. Dukiyar da aka same ta a sawwaƙe, amfaninta kaɗan ne.

22. Kada ka ɗaukar wa kanka fansa, ka dogara ga Ubangiji shi zai yi sakamako.

Karanta cikakken babi K. Mag 20