Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

K. Mag 19:23-29 Littafi Mai Tsarki (HAU)

23. Ka yi tsoron Ubangiji za ka yi tsawon rai, ka kuma sami biyan bukata, ba abin da zai cuce ka.

24. Waɗansu mutane sun cika lalaci, ko abincinsu ba su iya taunawa.

25. Za a hukunta mai fāriya saboda ya zama ishara ga mutanen da ba su san kome ba, mutum mai hikima yakan koya sa'ad da aka tsauta masa.

26. Sai marar kunya, marar mutunci suke wulakanta mahaifinsa, ko ya kori mahaifiyarsa daga gidansa.

27. Ɗana idan ka bar yin nazari za ka manta da abin da ka riga ka koya.

28. Ba gaskiya ga mashaidin da ya yi niyyar cutar wani. Mugaye suna ƙaunar yin mugunta.

29. Wawa mai fāriya hakika zai sha dūka.

Karanta cikakken babi K. Mag 19