Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

K. Mag 15:9-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

9. Ubangiji yana ƙin hanyoyin mugaye, amma yana ƙaunar mutumin da yake yin abin da yake daidai.

10. Idan ka yi abin da ba daidai ba, za ka sha hukunci sosai, za ka mutu idan ka ƙi yarda da tsautawa.

11. Ko lahira ba za ta hana Ubangiji ya san abin da yake can ba. Ƙaƙa fa mutum zai iya ɓoye wa Allah tunaninsa?

12. Mai girmankai ba ya so a tsauta masa. Faufau ba zai nemi shawara a wurin masu hikima ba.

13. Sa'ad da mutum yake murna yakan yi murmushi, amma sa'ad da yake baƙin ciki yakan yi nadama.

14. Mutum mai basira yana neman ilimi, amma dakikai, jahilcinsu ya wadace su.

15. Wahaltaccen mutum a ko yaushe, fama yake yi a zamansa, amma masu farin ciki suna zama da daɗin rai.

16. Gara a zauna da talauci da tsoron Ubangiji, da a sami dukiya game da wahala.

17. Gara cin mabunƙusa tare da waɗanda kake ƙauna, da ka ci abinci mai romo a inda ƙiyayya take.

18. Zafin rai yakan kawo jayayya, amma haƙuri yana kawo salama.

19. Idan kai rago ne za ka gamu da wahala a ko'ina, amma idan kai amintacce ne, ba za ka sha wahala ba.

20. Ɗa mai hikima yana faranta zuciyar mahaifinsa, amma wawa yana raina mahaifiyarsa.

21. Dakikai suna murna da wautarsu, amma mai hikima zai aikata abin da yake daidai.

22. Ka nemi dukan shawarwarin da ka iya ka samu, za ka yi nasara, idan ba tare da shawara ba, za ka fāɗi.

Karanta cikakken babi K. Mag 15