Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

K. Mag 12:6-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Maganganun mugaye na kisankai ne, amma kalmomin adalai sukan ceci waɗanda ake neman ransu.

7. Mugaye sukan gamu da faɗuwarsu, ba magāda, amma iyalan adalai sukan dawwama.

8. Idan kai haziƙi ne, za a yabe ka, amma idan kai dakiki ne, mutane za su raina ka.

9. Gara kana talakanka, kana neman abinci, da ka mai da kanka kai wani abu ne, alhali kuwa abin da za ka ci ya fi ƙarfinka.

10. Mutumin kirki yakan lura da dabbobinsa, amma mugaye sukan yi wa nasu ƙeta.

11. Manomin da yake aiki ƙwarai yana da isasshen abinci. Wauta ce a ɓatar da lokaci a kan aikin banza.

12. Iyakar abin da mugaye suke so, shi ne su sami muguntar da za su yi, amma adalai suna tsaye daram.

13. Maganganun mugun sukan zamar masa tarko, amma amintacce yakan fid da kansa daga cikin wahala.

14. Sakayyar mutum ta rataya ne a kan maganarsa da aikinsa, zai sami abin da ya cancance shi.

15. Wawa a kullum tsammani yake abin da yake yi daidai ne, amma masu hikima sukan kasa kunne ga shawara.

16. Sa'ad da wawa ya hasala, nan da nan kowa zai sani, amma mai la'akari ba zai nuna ya kula ba.

17. Sa'ad da ka faɗi gaskiya, ka yi adalci, amma ƙarairayi su ne jagorar aikata rashin adalci.

Karanta cikakken babi K. Mag 12