Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

K. Mag 10:17-32 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Mutumin da yake kasa kunne sa'ad da ake kwaɓarsa zai rayu, amma duk wanda bai yarda da kuskurensa ba yana cikin hatsari.

18. Mutumin da yake faɗar ƙarairayi maƙiyi ne, dukan wanda yake baza jitajita wawa ne.

19. Bisa ga yawan surutunka, mai yiwuwa ne ƙwarai ka yi zunubi, amma idan kai mai la'akari ne, sai ka yi shiru.

20. Kalmomin mutumin kirki suna kama da azurfa tsantsa, amma shawarwarin mugu ba su da wani amfani.

21. Kalmomin mutumin kirki za su amfani mutane da yawa, amma kana iya hallaka kanka da wauta.

22. Albarkar Ubangiji takan arzuta mutum, amma yawan aiki ba shi yake kawo arziki ba.

23. Wawa ne yake jin daɗin aikata mugunta, amma mai fasaha yana jin daɗin hikima.

24. Abin da mugun yake tsoro, shi yakan auko masa, amma adali yakan sami biyan bukatarsa.

25. Hadiri yakan taso ya wargaza mugaye, amma amintattu lafiya lau suke a ko yaushe.

26. Sam, kada ka sa malalaci ya yi maka wani abu, zai sa ka ka yi fushi, idanunka su cika da hawaye mai zafi.

27. Ka yi tsoron Ubangiji za ka rayu, ka yi tsawon rai, amma mugaye sukan mutu tun kwanansu bai ƙare ba.

28. Abin da mutanen kirki suke sa zuciya yakan kai su ga murna, amma mugaye ba su da wani abu da za su sa zuciya a kai.

29. Ubangiji yana kiyaye marasa laifi, amma yakan hallaka masu mugunta.

30. Kullayaumi adalai sukan yi zamansu lafiya, amma mugaye ba za su zauna a ƙasar ba.

31. Maganar adalai ta hikima ce, amma harshen da yake hurta mugunta, za a dakatar da shi.

32. Adalai sun san irin maganar da ta cancanta su faɗa, amma mugaye, kullum sukan faɗi maganar da za ta cutar.

Karanta cikakken babi K. Mag 10