Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Josh 9:15-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Joshuwa kuwa ya yi amana da su, ya yi musu alkawari zai bar su da rai. Shugabannin jama'a kuma suka rantse musu.

16. Amma a rana ta uku bayan da suka yi alkawari da su, suka ji cewa, su maĈ™wabtansu ne, suna zaune a cikinsu.

17. Sai Isra'ilawa suka kama hanyarsu a rana ta uku suka isa biranen mutanen, wato Gibeyon, da Kefira, da Biyerot, da Kiriyat-yeyarim.

18. Amma Isra'ilawa ba su kashe su ba, domin shugabannin jama'a sun rantse musu da sunan Ubangiji Allah na Isra'ila. Dukan jama'a kuwa suka yi gunaguni a kan shugabannin.

Karanta cikakken babi Josh 9