Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Josh 24:26-28 Littafi Mai Tsarki (HAU)

26. Ya kuwa rubuta waɗannan kalmomi a littafin Shari'ar Ubangiji. Ya kuma ɗauki wani babban dutse, ya kafa a ƙarƙashin itacen oak a wuri mai tsarki na Ubangiji.

27. Sai ya ce wa jama'a, “Wannan dutse shi ne shaida a kanmu, gama ya ji dukan abin da Ubangiji ya faɗa mana, domin haka zai zama shaida a kanku, don kada ku yi wa Allahnku ƙarya.”

28. Joshuwa kuwa ya sallami jama'ar, kowane mutum ya koma wurin gādonsa.

Karanta cikakken babi Josh 24