Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 6:4-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. Amon muryoyinsu ya sa harsashin ginin Haikali ya girgiɗa, Haikalin kansa kuma ya game da hayaƙi.

5. Sai na ce, “Sa zuciyata ya ƙare! Na shiga uku! Kowace maganar da ta fito bakina zunubi ce, ina zaune a tsakanin mutane waɗanda duk maganarsu zunubi ce, ba ta da tsarki. Amma yanzu da idona na ga Sarki, Ubangiji Mai Runduna!”

6. Sa'an nan ɗaya daga cikin talikan ya tashi ya sauko zuwa gare ni, yana riƙe da garwashin wuta wanda ya ɗauko da arautaki daga bagade.

7. Ya taɓa leɓunana da garwashin wutar ya ce, “Wannan ya taɓa leɓunanka, yanzu fa an kawar da laifofinka, an kuma gafarta maka zunubanka.”

8. Sai na ji Ubangiji yana cewa, “Wa zan aika? Wa zai zama manzonmu?”Sai na amsa na ce, “Ga ni! Ka aike ni!”

Karanta cikakken babi Ish 6