Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 50:7-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Amma zaginsu ba zai yi mini ƙari ba,Gama Ubangiji Allah yana taimakona.Na ƙarfafa kaina domin in jure da su.Na sani ba zan kunyata ba,

8. Gama Allah yana kusa,Zai tabbatar da ni, marar laifi ne,Ko akwai wanda zai iya kawo ƙararraki game da ni?Bari mu je ɗakin shari'a tare!Bari ya kawo ƙararrakinsa!

9. Ubangiji kansa zai kāre ni,Wa zai iya tabbatar da ni mai laifi ne?Dukan waɗanda suke sarana za su shuɗe,Za su shuɗe kamar tufar da asu ya cinye!

10. Ku duka da kuke tsoron Ubangiji,Kuna kuma biyayya da kalmomin bawansa,Zai yiwu hanyar da kuke bi ta yi duhu ƙwarai,Amma ku dogara ga Ubangiji, ku jingina ga Allahnku.

11. Dukanku da kuke ƙulle-ƙullen hallaka junaƘulle-ƙullenku za su hallaka ku!Ubangiji kansa zai sa wannan ya faru,Za ku gamu da mummunar ƙaddara.

Karanta cikakken babi Ish 50