Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 48:8-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Na sani ba za a iya gaskata ku ba,Tun daga haihuwarku kuma an san ku da tayarwa.Shi ya sa ba ku taɓa jin wannan ba ko kaɗan,Ko kalma ɗaya ba ta taɓa shiga kunnenku ba.

9. “Saboda mutane su yi yabon sunanaShi ya sa nake danne fushina,Ina kuma ɓoye shi, kada in hallaka ku.

10. Na gwada ku da wutar wahala,Kamar yadda ake tace azurfa a tanda,Amma na tarar ba ku da amfani.

11. Abin da na yi, na yi shi don kaina ne,Ba zan bari a rasa girmama sunana ba,Ko kuwa wani dabam ya sami ɗaukakaWadda take tawa ce, ni kaɗai.”

12. “Ku kasa kunne gare ni, ya Isra'ila, jama'ar da na kira!Ni ne Allah, farko, da ƙarshe, Allah Makaɗaici!

13. Dantsena ne ya kafa harsashin ginin duniya,Ya kuma shimfiɗa sammai.Lokacin da na kira duniya da sararin sama,Sukan zo nan da nan, su gabatar da kansu!

Karanta cikakken babi Ish 48