Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 45:1-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sairus shi ne zaɓaɓɓen sarki na Ubangiji!Ubangiji ya sa shi ya ci al'ummai,Ya aike shi ya tuɓe ikon sarakuna,Ubangiji zai buɗe masa ƙofofin birni.Ubangiji ya ce wa Sairus,

2. “Ni kaina zan shirya hanya dominka,Ina baji duwatsu da tuddai.Zan kakkarye ƙyamaren tagulla,In kuma daddatse gagara badau na baƙin ƙarfe.

3. Zan ba ka dukiya daga cikin duhu, a asirtattun wurare,Sa'an nan za ka sani ni ne Ubangiji,Allah na Isra'ila kuma, shi ne ya zaɓe ka.

4. Na sa ka domin ka taimaki bawana Isra'ila,Jama'ar da ni na zaɓa.Na ba ka girma mai yawa,Ko da yake kai ba ka san ni ba.

5. “Ni ne Ubangiji, ba wani Allah sai ni.Zan ba ka irin ƙarfin da kake bukata,Ko da yake kai ba ka san ni ba.

6. Na yi wannan domin dukan waɗanda suke daga wannan bangon duniya zuwa wancanSu sani ni ne Ubangiji,Ba kuwa wani Allah sai ni.

Karanta cikakken babi Ish 45