Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 43:6-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Zan faɗa wa kudu su bar su su tafi,Arewa kuma kada su riƙe su a can.Bari mutanena su komo daga manisantan ƙasashe,Daga kowane sashi na duniya.

7. Su mutanena ne, na kaina,Na kuwa halicce su don su girmama ni.”

8. Allah ya ce,“Kirawo mutanena a ɗakin shari'a.Suna da idanu, amma makafi ne,Suna da kunnuwa, amma kurame ne!

9. Kirawo sauran al'umma, su zo ga shari'a.A cikin allolinsu wane zai iya faɗar abin da yake a gaba?A cikinsu wa ya yi hurci a kan abin da yake faruwa yanzu?Bari waɗannan alloli su kawo shaidunsuDon su tabbatar daidai suke,Su shaida gaskiyar maganganunsu.

10. “Ya jama'ar Isra'ila, ku ne shaiduna,Na zaɓe ku al'umma, baiwata,Domin ku san ni, ku gaskata ni,Ku kuma fahimta, ni kaɗai ne Allah.In banda ni ba wani Allah,Ba a taɓa yin wani ba,Ba kuwa za a yi ba.

11. “Ni kaɗai ne Ubangiji,Ni kaɗai ne wanda yake da ikon yin ceto.

12. Na faɗi abin da zai faruSa'an nan na zo domin taimakonku.Ba wani gunkin da ya taɓa yin haka,Ku ne shaiduna.

Karanta cikakken babi Ish 43