Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 42:17-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Dukan waɗanda suke dogara ga gumaka,Masu kiran siffofi allolinsu,Za a ƙasƙantar da su, su kuma sha kunya.”

18. Ubangiji ya ce,“Ku kasa kunne, ya ku kurame!Ku duba da kyau sosai, ku makafi!

19. Akwai sauran wanda ya fi bawana makanta,Ko wanda ya fi manzona kurunta, wato wanda na aiko?

20. Isra'ila, kun ga abu da yawa,Amma bai zama da ma'ana a gare ku ba ko kaɗan.Kuna da kunnuwan da za ku ji,Amma a ainihi me kuka ji?”

21. Ubangiji shi Allah ne da ya ƙosa ya yi ceto saboda gaskiyarsa,Saboda haka yana so a girmama koyarwarsa,

Karanta cikakken babi Ish 42