Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 42:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ubangiji ya ce,“Ga bawana, wanda na ƙarfafa,Wanda na zaɓa, wanda nake jin daɗinsa.Na cika shi da ikona,Zai kuwa kawo shari'ar gaskiya ga dukan al'ummai.

2. Ba zai yi tsawa ko ya ta da muryarsa ba,Ko ya yi jawabi da babbar murya a tituna.

3. Zai lallaɓi marasa ƙarfi,Ya nuna alheri ga tafkakku.Zai kawo madawwamiyar gaskiya ga duka.

4. Ba zai fid da zuciya ko ya karai ba,Zai kuma kafa gaskiya a duniya,Manisantan ƙasashe sun zaƙu, suna jiran koyarwarsa.”

5. Allah ya halicci sammai ya kuma shimfiɗa su,Ya yi duniya, da dukan masu rai nata,Ya ba da rai da numfashi ga dukan mutanenta.Yanzu kuwa Ubangiji Allah ya ce wa bawansa,

Karanta cikakken babi Ish 42