Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 41:10-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Kada ka ji tsoro, ina tare da kai,Ni ne Allahnka, kada ka bar kome ya firgita ka.Zan sa ka yi ƙarfi, in kuma taimake ka,Zan kiyaye ka, in cece ka.

11. “Su waɗanda suke fushi da ku, ku jama'ata,Za a ƙasƙantar da su su ji kunya.Waɗanda suke faɗa da ku kuwa za su mutu.

12. Za ku neme su, amma ba za ku same su ba,Wato waɗanda suke gāba da ku.Waɗanda suka kama yaƙi da ku,Za su shuɗe daga duniya.

13. Ni ne Ubangiji Allahnku,Na ƙarfafa ku, na kuwa faɗa muku,‘Kada ku ji tsoro, ni zan taimake ku.’ ”

Karanta cikakken babi Ish 41