15. Al'ummai ba kome ba ne a wurin Ubangiji,Ba su fi ɗigon ruwa ba,Manisantan tsibirai ba su fi ƙura nauyi ba.
16. Dukan dabbobin da yake a jejin LebanonBa su isa hadaya guda ga Allahnmu ba,Itatuwan jejin kuma ba su isa a hura wuta da su ba.
17. Al'ummai ba kome ba ne ko kaɗan a gare shi.
18. Da wa za a iya kwatanta Allah?Wa zai iya faɗar yadda yake?