Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 2:13-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. Zai hallaka dogayen itatuwan al'ul na Lebanon, da dukan itatuwan oak na ƙasar Bashan.

14. Zai baje duwatsu da tuddai masu tsayi,

15. da kowace doguwar hasumiya, da ganuwar kowace kagara.

16. Zai nutsar da jiragen ruwa mafi girma mafi kyau.

17. Girmankan ɗan adam zai ƙare, za a hallakar da fāriyar ɗan adam, Ubangiji ne kaɗai za a ɗaukaka sa'ad da wannan rana ta yi,

18. za a shafe gumaka ƙaƙaf.

19. Mutane za su ɓuya a kogwannin duwatsu, ko su haƙa ramummuka a ƙasa, suna ƙoƙarin tserewa daga fushin Ubangiji, ko su ɓuya daga ikonsa da ɗaukakarsa, sa'ad da ya zo domin ya girgiza duniya.

20. Sa'ad da wannan rana ta yi za su zubar da gumakan da suka yi na zinariya da azurfa, za su bar wa ɓeraye da jemagu.

Karanta cikakken babi Ish 2