Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 14:22-28 Littafi Mai Tsarki (HAU)

22. Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Zan fāɗa wa Babila da yaƙi, in lalata ta, ba abin da zan bari, ko yara, ba wanda zai ragu. Ni, Ubangiji, na faɗi wannan.

23. Zan su Babila ta zama fadama, mujiyoyi za su zauna a can. Zan kuwa share Babila da tsintsiyar da za ta share kome. Ni, Ubangiji Mai Runduna, na faɗa.”

24. Ubangiji Mai Runduna ya rantse, ya ce, “Abin da na riga na shirya, haka zai faru. Abin da na yi niyyar yi, za a yi.

25. Zan hallaka Assuriyawa a ƙasata ta Isra'ila, in tattake su a kan duwatsuna. Zan 'yantar da jama'ata daga karkiyar Assuriyawa, daga nauyin da suka tilasta musu su ɗauka.

26. Abin da na shirya zan yi wa duniya, shi ne in miƙa hannuna domin in hukunta wa al'ummai.”

27. Ubangiji Mai Runduna ne ya ƙudura ya yi wannan, ya miƙa dantsensa don ya yi hukunci, ba kuwa mai iya hana shi.

28. Wannan shi ne jawabin da aka yi shelarsa a shekarar da sarki Ahaz ya rasu.

Karanta cikakken babi Ish 14