Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 8:5-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Me ya sa, mutanen nan naUrushalima suke ratsewa, sukekomawa baya kullayaumin?Sun riƙe ƙarya kan-kanSun ƙi komowa.

6. Na kula sosai, na saurara,Amma ba wanda ya faɗi watamaganar kirki,Ba wanda ya taɓa barin muguntarsa,Kowa cewa yake, “Me na yi?”Kamar dokin da ya kutsa kai cikinfagen fama.

7. Ko shamuwa ta sararin sama ma, tasan lokatanta,Tattabara da tsattsewa, da gaurakasuna kiyaye lokacin komowarsu.Amma mutanena ba su san dokokinaba.

8. Ƙaƙa za ku ce, “Muna da hikima,Dokar Ubangiji tana tare da mu”?Ga shi kuwa, alkalamin ƙarya namagatakarda, ya yi ƙarya.

9. Za a kunyatar da masu hikima.Za su tsorata, za a kuma tafi da su.Ga shi, sun ƙi maganar Ubangiji.Wace hikima suke da ita?

10. Saboda haka zan ba da matansu gawaɗansu,Gonakinsu kuma ga waɗanda sukecinsu da yaƙi,Saboda tun daga ƙarami har zuwababbaKowannensu yana haɗamar cinmuguwar riba,Tun daga annabawa zuwa firistociKowannensu aikata ha'inci yake yi.

11. Sun warkar da raunin mutanenasama sama,Suna cewa, “Lafiya, lafiya,” alhalikuwa ba lafiya.

12. Ko sun ji kunyaSa'ad da suka aikata ayyuka masubanƙyama?A'a, ba su ji kunya ba ko kaɗan,Fuskarsu ko gezau ba ta yi ba.Domin haka za su faɗi tare dafāɗaɗɗu,Sa'ad da na hukunta su, za a ci su dayaƙi.Ni Ubangiji na faɗa.’

13. “Ni Ubangiji na ce,‘Sa'ad da zan tattara su kamaramfanin gona,Sai na tarar ba 'ya'ya a kurangarinabi,Ba 'ya'ya kuma a itacen ɓaure,Har ganyayen ma sun bushe.Abin da na ba su kuma ya kuɓucemusu.Ni Ubangiji na faɗa.’ ”

Karanta cikakken babi Irm 8