Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 44:16-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. “Ba za mu kasa kunne ga jawabin da kake yi mana da sunan Ubangiji ba!

17. Za mu aikata dukan abin da muka faɗa. Za mu miƙa wa gunkiyan nan, wato sarauniyar sama, hadayu, da hadayu na sha kamar yadda kakanninmu, da shugabanninmu suka yi a garuruwan Yahuza, da kan titunan Urushalima. A lokacin kuwa muna da abinci a wadace, muka arzuta, ba wata wahala.

18. Amma tun da muka daina miƙa wa sarauniyar sama hadayu, da hadayu na sha, ba mu da kome, sai dai takobi da yunwa suke kashe mu.”

19. Mata kuma suka ce, “Sa'ad da muka toya waina ga siffar sarauniyar sama, muka miƙa mata hadayu, da hadayu na sha, ai, mazanmu sun goyi bayan abin da muka yi.”

Karanta cikakken babi Irm 44