Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 31:36-40 Littafi Mai Tsarki (HAU)

36. “Idan dai wannan kafaffiyar ka'idata daina aiki a gabana,Ni Ubangiji na faɗa,To, ashe, zuriyar Isra'ila za ta dainazama al'umma a gabana ke nanhar abada.

37. Idan a iya auna sammai a kuma iyabincike tushen duniya a ƙarƙas,To, ashe, zan watsar da dukanzuriyar Isra'ila ke nan sabodadukan abin da suka yi,Ni Ubangiji na faɗa.

38. “Ga shi, kwanaki suna zuwa da za a sāke gina birnin domin Ubangiji, ni Ubangiji na faɗa, tun daga hasumiyar Hananel zuwa yamma, har zuwa Ƙofar Kan Kusurwa.

39. Sa'an nan ma'aunin zai daɗa gaba, har ya kai tudun Gareb, sa'an nan ya nausa zuwa Gowa.

40. Dukan filin kwarin gawawwaki da toka, da dukan filaye har zuwa rafin Kidron zuwa kan kusurwar Ƙofar Doki wajen gabas, za su zama mai tsarki ga Ubangiji. Ba za a ƙara tumɓuke shi ko a rushe shi ba har abada.”

Karanta cikakken babi Irm 31