Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 3:19-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

19. “Isra'ila, na yi niyya in karɓe kukamar ɗana,In gādar muku da kyakkyawarƙasaMafi kyau a dukan duniya.Na zaci za ku ce ni ne mahaifinku,Ba za ku ƙara rabuwa da bina ba.

20. Hakika kamar yadda mace mararaminci takan bar mijinta,Haka kun zama marar aminci a gareni, ya jama'ar Isra'ila.Ni Ubangiji, na faɗa.”

21. An ji murya a kan filayen tuddai,Kūka da roƙo ne na 'ya'yanIsra'ila maza,Domin sun rabu da hanyarsu,Sun manta da Ubangiji Allahnsu.

22. “Ku juyo ku marasa aminci,Zan warkar da rashin amincinku.”“To, ga shi, mun zo gare ka,Gama kai ne Ubangiji Allahnmu,

Karanta cikakken babi Irm 3