Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 18:1-7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ubangiji ya yi magana da Irmiya ya ce,

2. “Ka tashi, ka gangara zuwa gidan maginin tukwane, a can zan yi maka magana.”

3. Sai na gangara zuwa gidan maginin tukwanen, na iske shi yana ginin tukwane a kan na'urar ginin tukwanen.

4. Abin da yake ginawa ya lalace a hannunsa, sai ya sāke gina wani abu dabam da yumɓu ɗin, yadda ya ga dama.

5. Sa'an nan Ubangiji ya ce mini,

6. “Ya jama'ar Isra'ila, ashe, ba zan yi da ku kamar yadda maginin tukwanen nan ya yi ba? Duba, kamar yadda yumɓu yake a hannun maginin tukwane, haka kuke a hannuna, ya ku jama'ar Isra'ila.

7. A duk lokacin da na ce zan tumɓuke, in kakkarya in hallaka wata al'umma, ko wani mulki,

Karanta cikakken babi Irm 18