Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 10:15-25 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Su ba kome ba ne, aikin ruɗami ne,A lokacin da za a hukunta su za sulalace.

16. Gama shi ba kamar waɗannan yakeba,Shi na Yakubu ne.Shi ne ya yi dukan kome,Kabilan Isra'ilawa gādonsa,Sunansa Ubangiji Mai Runduna.

17. Ku tattara kayayyakinku,Ku mazaunan wurin da aka kewayeda yaƙi.

18. Gama haka Ubangiji ya ce,“Ga shi, ina jefar da mazaunanƙasar daga ƙasarsu a wannanlokaci,Zan kawo musu wahala, za su kuwaji jiki.”

19. Tawa ta ƙare, saboda raunin da akayi mini.Raunina mai tsanani ne,Amma na ce, lalle wannan azaba ce,Tilas in daure da ita.

20. An lalatar da alfarwata,Dukan igiyoyi sun tsintsinke,'Ya'yana maza sun bar ni, ba sunan.Ba wanda zai kafa mini alfarwataYa kuma rataya labulena.

21. Makiyayan dakikai ne,Ba su roƙi Ubangiji ba,Don haka ba su sami wadata ba,An watsa dukan garkensu.

22. Ku ji fa, an ji ƙishin-ƙishin! Ga shikuma, yana tafe.Akwai babban hargitsin da ya fitodaga arewa,Don a mai da biranen Yahuza kufai,wurin zaman diloli.

23. “Ya Ubangiji, na sani al'amuranmutum ba a hannunsa suke ba,Ba mutum ne yake kiyaye takawarsaba

24. Ka tsauta mini, ya Ubangiji, ammada adalcinka,Ba da fushinka ba, don kada kawofinta ni.

25. Ka kwarara hasalarka a kan sauranal'umma da ba su san ka ba,Da a kan jama'ar da ba su kiransunanka,Gama sun cinye Yakubu,Sun cinye shi, sun haɗiye shi,Sun kuma mai da wurin zamansakufai.”

Karanta cikakken babi Irm 10