Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Fit 9:30-35 Littafi Mai Tsarki (HAU)

30. Amma dai na sani, da kai da fādawanka, har wa yau ba ku ji tsoron Ubangiji Allah ba tukuna.”

31. Rama da sha'ir suka lalace, gama sha'ir ya riga ya nuna, rama kuwa tana huda.

32. Amma alkama da maiwa ba su lalace ba, gama kakarsu ba ta yi ba tukuna.

33. Sai Musa ya fita daga wurin Fir'auna ya rabu da birnin. Ya yi addu'a ga Ubangiji sai walƙiya da ƙanƙara suka tsaya, kwararowar ruwa kuma ta ɗauke.

34. Da Fir'auna ya ga an ɗauke ruwa, da ƙanƙara, da kuma walƙiya, sai ya sāke yin zunubi, ya taurare zuciyarsa, da shi da fādawansa.

35. Zuciyar Fir'auna ta taurare, har ya ƙi sakin Isra'ilawa kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa ta bakin Musa.

Karanta cikakken babi Fit 9