Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Fit 36:4-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. Sai masu hikiman da suke yin aiki na alfarwa ta sujada suka ɗan dakatar da aiki suka tafi wurin Musa.

5. Suka ce masa, “Jama'a suna ta kawo sadaka fiye da abin da ake bukata domin aikin da Ubangiji ya umarta a yi.”

6. Sai Musa ya umarce su su yi shela a zango cewa, “Kada wata mace ko wani namiji ya sāke kawo sadaka don aikin alfarwa ta sujada.” Sai jama'a suka daina kawowa.

7. Gama abin da aka kawo ya isa yin aikin, har da ragi.

8. Sai dukan mutane masu gwaninta daga cikin ma'aikatan, suka yi alfarwa da labule goma. An yi labulen da lallausan zaren lilin na shuɗi, da shunayya, da mulufi. Aka yi wa labulen zānen kerubobi na gwaninta.

9. Tsawon kowane labule kamu ashirin da takwas, fāɗinsa kuma kamu huɗu ne. Dukan labulen girmansu ɗaya ne.

10. Ya ɗinɗinke labule biyar a harhaɗe, haka kuma ya yi da sauran labule biyar.

11. Sai ya sa shuɗɗan hantuna a karbun labule na fari da na biyu.

12. Ya sa hantuna hamsin a karbun labule na fari, haka kuma ya sa na biyun. Dukan hantunan suna daura da juna.

Karanta cikakken babi Fit 36