18. “Kada a bar mace mai sihiri ta rayu.
19. “Duk wanda ya kwana da dabba, lalle kashe shi za a yi.
20. “Wanda ya miƙa hadaya ga wani allah, ba ga Ubangiji ba, sai a hallaka shi ɗungum.
21. “Kada ku wulakanta baƙo ko ku zalunce shi, gama dā ku baƙi ne a ƙasar Masar.
22. Kada ku ci zalun marayu da gwauraye.