11. Gama cikin kwana shida Ubangiji ya yi sama, da duniya, da teku, da dukan abin da yake cikinsu, amma a rana ta bakwai ya huta. Soboda haka Ubangiji ya keɓe ranar Asabar, ya tsarkake ta.
12. “Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, domin ka yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka.
13. “Kada ka yi kisankai.
14. “Kada ka yi zina.
15. “Kada ka yi sata.
16. “Kada ka ɓāta sunan maƙwabcinka.