Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Fit 15:1-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Musa da jama'ar Isra'ila suka raira wannan waƙa ga Ubangiji suka ce,“Zan raira waƙa ga Ubangiji, gama ya ci gawurtacciyar nasara,Dawakai da mahayansu ya jefar cikin bahar.

2. Ubangiji ne ƙarfina da mafakata,Shi ne wanda ya cece ni.Wannan ne Allahna, zan yabe shi,Allah na kakana, zan ɗaukaka shi.

3. Ubangiji mayaƙi ne,Yahweh ne sunansa.

4. “Karusan Fir'auna da rundunarsa, ya jefar cikin bahar,Zaɓaɓɓun jarumawansa ya nutsar da su cikin Bahar Maliya.

5. Rigyawa ta rufe su,Suka nutse cikin zurfi kamar dutse.

6. Ya Ubangiji dantsen damanka, mai iko ne,Ya Ubangiji, dantsen damanka ya ragargaza magabta.

7. Cikin girman ɗaukakarka, ka kā da maƙiyanka, ka aika da hasalarka,Ka cinye su kamar ciyawa.

8. Da hucin numfashin hancinka ruwa ya tattaru,Rigyawa ta tsaya kamar tudu,Zurfafan ruwa suka daskare a tsakiyar bahar.

9. Magabcin ya ce, ‘Zan bi, in kama su, in raba ganima,Muradina a kansu zai biya, zan zare takobina, hannuna zai hallaka su.’

10. Ka hura iskarka, bahar ta rufe su, suka nutse kamar darma cikin manyan ruwaye.

11. “Ya Ubangiji, wane ne kamarka a cikin alloli?Wa yake kamarka a cikin ɗaukaka da tsarki?Mai banrazana cikin mafifitan ayyuka, mai aikata mu'ujizai.

12. Ka miƙa dantsen damanka, ƙasa ta haɗiye su.

13. Da tabbatacciyar ƙaunarka, ka bi da jama'arka da ka fansa,Ka bi da su da ƙarfinka zuwa tsattsarkan mazauninka.

14. Al'ummai suka ji suka yi rawar jiki,Tsoro ya kama mazaunan Filistiya.

15. Sarakunan Edom suka tsorata,Shugabannin Mowab suna rawar jiki,Dukan mazaunan Kan'ana sun narke.

16. Tsoro da razana sun aukar musu,Ta wurin ikonka suka tsaya cik kamar dutse,Har jama'arka, ya Ubangiji, suka haye,I, jama'arka, ya Ubangiji, suka haye,

Karanta cikakken babi Fit 15