Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Far 48:18-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. Sai Yusufu ya ce wa mahaifinsa, “Ba haka ba ne baba, gama wannan ne ɗan fari. Sa hannunka na dama a bisa kansa.”

19. Amma mahaifinsa ya ƙi, ya ce, “Na sani, ɗana, na sani, shi ma zai zama al'umma, zai ƙasaita, duk da haka ƙanensa zai fi shi ƙasaita, zuriyarsa kuwa za ta zama taron al'ummai.”

20. Ya sa musu albarka a wannan rana, yana cewa,“Ta gare ku Isra'ila za su sa albarkada cewa,‘Allah ya maishe ku kamar Ifraimuda Manassa.’ ”Da haka ya sa Ifraimu gaba da Manassa.

Karanta cikakken babi Far 48