Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Far 33:15-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Sai Isuwa ya ce, “Bari in bar waɗansu daga cikin mutanen da suke tare da ni, a wurinka.”Amma Yakubu ya ce, “Ka kyauta ƙwarai, amma ba na bukatar haka, ya shugaba.”

16. A ran nan Isuwa ya koma a kan hanyarsa zuwa Seyir.

17. Yakubu ya kama hanya zuwa Sukkot, ya kuwa gina wa kansa gida, ya yi wa shanunsa garke. Saboda haka aka sa wa wurin suna Sukkot.

18. Yakubu kuwa ya kai birnin Shalem wanda yake ƙasar Kan'ana lafiya, a kan hanyarsa daga Fadan-aram, ya kuwa yi zango a ƙofar birnin.

19. Ya kuma sayi yankin saura inda ya kafa alfarwarsa daga 'ya'yan Hamor, mahaifin Shekem, a bakin azurfa ɗari.

20. A wurin ya gina bagade ya sa masa suna El-Elohe-Isra-el.

Karanta cikakken babi Far 33