Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Far 32:18-32 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. Sa'an nan sai ku ce, ‘Na Yakubu baranka ne, kyauta ce zuwa ga shugabana Isuwa, ga shi nan ma biye da mu.’ ”

19. Da haka nan ya umarci na biyu da na uku da dukan waɗanda suke korar garkunan, ya ce, “Sai ku faɗa wa Isuwa daidai haka nan.

20. Ku kuma ce, ‘Ga shi ma, Yakubu ɗan'uwanka yana biye da mu.’ ” Gama, cikin tunaninsa ya ce, “Ya yiwu in gamshe shi da kyautar da ta riga ni gaba, daga baya in ga fuskarsa, watakila ya karɓe ni.”

21. Saboda haka kyautar ta yi gaba, shi kansa kuwa a daren, ya sauka a zango.

22. A wannan dare kuwa ya tashi ya ɗauki matansa biyu, da kuyanginsa biyu da 'ya'yansa goma sha ɗaya ya haye mashigin Jabbok.

23. Ya ɗauke su ya haye da su rafi, haka kuma ya yi da dukan abin da yake da shi.

24. Aka bar Yakubu shi kaɗai.Sai wani mutum ya kama shi da kokawa har wayewar gari.

25. Sa'ad da mutumin ya ga bai rinjayi Yakubu ba sai ya taɓa kwarin kwatangwalonsa, sai gaɓar kwatangwalon Yakubu ta gulle a lokacin da yake kokawa da shi.

26. Sa'an nan sai mutumin ya ce, “Ka bar ni in tafi, gama gari na wayewa.”Amma Yakubu ya ce, “Ba zan bar ka ka tafi ba, sai ka sa mini albarka.”

27. Sai ya ce masa, “Yaya sunanka?”Ya ce, “Yakubu.”

28. Sai ya ce, “Ba za a ƙara kiranka da suna Yakubu ba, amma za a kira ka Isra'ila, gama ka yi kokawa da Allah da mutane, ka kuwa yi rinjaye.”

29. Sa'an nan Yakubu ya tambaye shi, “Ina roƙonka, faɗa mini sunanka.”Amma ya ce, “Don me kake tambayar sunana?” A nan mutumin ya sa masa albarka.

30. Saboda haka Yakubu ya sa wa wurin suna Feniyel, yana cewa, “Gama na ga Allah fuska da fuska, duk da haka ban mutu ba.”

31. Rana ta yi sama a sa'ad da Yakubu ya wuce Feniyel domin yana ɗingishi saboda kwatangwalonsa.

32. Saboda haka, har wa yau, Isra'ilawa ba sā cin jijiyar kwatangwalo wadda take a kwarin kwatangwalo, domin an taɓi kwarin kwatangwalon Yakubu ta jijiyar kwatangwalo.

Karanta cikakken babi Far 32