Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Far 27:16-26 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. fatun 'yan awakin kuwa ta naɗe wa hannuwansa, da sashen dokin wuyansa mai sulɓi.

17. Sai ta bai wa ɗanta, Yakubu, abinci mai daɗin ci da gurasar da ta shirya.

18. Ya kuwa shiga wurin mahaifinsa, ya ce, “Baba.”Mahaifin ya ce, “Ga ni, wane ne kai, ya ɗana?”

19. Yakubu ya ce wa mahaifinsa, “Ni ne Isuwa ɗan farinka. Na yi yadda ka faɗa mini, in ka yarda ka tashi ka ci naman da na harbo, domin ka sa mini albarka.”

20. Amma Ishaku ya ce wa ɗansa, “Ƙaƙa aka yi ka same shi da sauri haka, ɗana?”Sai ya amsa, “Domin Ubangiji, Allahnka, ya ba ni sa'a.”

21. Ishaku kuwa ya ce wa Yakubu, “Matso kusa in ka yarda, don in lallaluba ka, ɗana, domin in hakikance ko kai ne ɗana Isuwa, ko babu.”

22. Saboda haka Yakubu ya matsa kusa da Ishaku mahaifinsa, sai ya lallaluba shi, ya ce, “Murya, muryar Yakubu ce, amma hannuwa, hannuwan Isuwa ne.”

23. Amma bai gane shi ba, gama hannuwansa gargasa ne kamar hannuwan ɗan'uwansa Isuwa, saboda haka ya sa masa albarka.

24. Ya ce, “Hakika, kai ne ɗana Isuwa?”Ya amsa, “Ni ne.”

25. Ya ce, “Kawo mini naman da ka harbo, in ci in sa maka albarka.” Sai ya kawo masa, ya kuwa ci, ya kawo masa ruwan inabi, ya sha.

26. Mahaifinsa Ishaku kuwa ya ce masa, “Zo kusa ka sumbace ni, ɗana.”

Karanta cikakken babi Far 27