Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Far 27:15-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Rifkatu ta ɗauki riguna mafi kyau na babban ɗanta Isuwa waɗanda suke wurinta cikin gida, ta kuwa sa wa Yakubu ƙaramin ɗanta su,

16. fatun 'yan awakin kuwa ta naɗe wa hannuwansa, da sashen dokin wuyansa mai sulɓi.

17. Sai ta bai wa ɗanta, Yakubu, abinci mai daɗin ci da gurasar da ta shirya.

18. Ya kuwa shiga wurin mahaifinsa, ya ce, “Baba.”Mahaifin ya ce, “Ga ni, wane ne kai, ya ɗana?”

Karanta cikakken babi Far 27