Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Far 26:28-35 Littafi Mai Tsarki (HAU)

28. Suka ce, “Lalle, mun gani a fili Ubangiji yana tare da kai, saboda haka muke cewa bari rantsuwa ta kasance tsakaninmu da kai, bari kuma mu ƙulla alkawari da kai,

29. cewa ba za ka cuce mu ba, daidai kamar yadda ba mu taɓe ka ba, ba mu yi maka kome ba sai alheri, muka kuwa sallame ka cikin salama. Yanzu, kai albarkatacce ne na Ubangiji.”

30. Sai ya shirya musu liyafa, suka ci suka sha.

31. Suka tashi tun da sassafe suka rantse wa juna, Ishaku ya sallame su, suka tafi cikin salama.

32. Ya zama kuwa a wannan rana, barorin Ishaku suka zo suka faɗa masa zancen rijiyar da suka haƙa, suka ce masa, “Mun sami ruwa.”

33. Ya sa mata suna Sheba, domin haka har yau sunan birnin Biyer-sheba.

34. Sa'ad da Isuwa yake da shekara arba'in, ya auro Judit, 'yar Biyeri Bahitte, da Basemat 'yar Elon Bahitte,

35. suka baƙanta wa Ishaku da Rifkatu rai.

Karanta cikakken babi Far 26